Isa ga babban shafi

Yara mata sama da miliyan 7 ne aka dakile wa damar samun ilimi a Najeriya

Asusun Kula da  Kananan Yara  na Majalisar Dinkin Duniya, wato UNICEF, ya ce yara mata miliyan 7 da dubu dari 6 ne aka dakile wa damar samun ilimi a Najeriya, kuma galibin su daga arewacin kasar su ke.

Wata karamar yarinya a nahiyar Afrika, yayin gudanar da talla a gefen hanya.
Wata karamar yarinya a nahiyar Afrika, yayin gudanar da talla a gefen hanya. Reuters
Talla

Wakiliyar asusun a Najeriya, Ms Cristian Munduate ce ta sanar da haka a Kano, da ke arewacin kasar, a yayin bikin tunawa da ‘Ranar ‘Yaya Mata ta Duniya ta shekarar 2023’, wanda aka yi a fadar gwamnatin jihar.

Ta ce a yayin da  nasaroroin da ‘yaya mata ke samu ke bada kwarin gwiwa, lamarin da ke tayar da hankali shi ne rashin bai wa miliyoyin ‘yaya mata damar samun ilimi, matsalar da aka fi samu a arewacin Najeriya.

Ta ce wani abin tashin hankali a nan shine yadda Najeriya ke da kaso 15 na adadin yaran da aka ba sa zuwa makaranta a fadin duniya, tana mai cewa wannan kalubale ne babba.

Ta kara da cewa yayin da jihar Kano ke a matsayi na biyu wajen yawan ‘yaya  mata da  ba sa makaranta a Najeriya, akwai bukatar  jaddada mahimmanci ilimi  a matsayin makamin da ba kawai yake yakar jahilci ba, har ma da wargaza kangin talauci.

Tun da farko a wata tattaunawa da dalibai mata suka yi, sun  yi bayani a game da dimbim kalubalen da ke kasancewa karfen kafa wajen neman ilimin ‘yaya mata, da kuma bukatar damawa da mata a bangarori dabam-dabam na rayuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.