Nijar-Faransa-Algeriya
Yan Kungiyar Al-Qaeda Sun Sako Dan Algeriya
A kasar Janhuriyar Nijar, wata kungiya da ake ganin reshe ce ta Kungiyar Al-Qaeda dake garkuwa da wasu 'yan-kasar waje biyu, sun sako daya, wanda dan kasar Algeriya ne, amma kuma dayan wanda dan kasar Faransa ne na hannun kungiyar.Majiyoyi sun fadi cewa dan kasar Algeriyan har ya koma kasarsu daga kasar ta Nijar.Bayanai na nuna cewa Dan kasar Algeriyan dreba ne na Bafaranshen mai shekaru samada 70.Saidai kuma wasu majiyoyin Tsaro na kasar Nijar na cewa Bafaranshen na can kasar Mali ne ake garkuwa dashi.Babu dai wata kungiya data amsa cewa itace ta sace mutanen biyu.
Wallafawa ranar: