Isa ga babban shafi
Nijar

Ambaliyar ruwa ta yi wa sama mutane dubu 20 illa a Nijar

Akalla mutane 4 ne suka rasa rayukansu yayin da sama da dubu 20 suka rasa muhallinsu a wata ambaliyar ruwa da ta auku a Jamhuriyar Niger sakamakon ruwan sama da aka dau tsawon makonin ana tafkawa.

Halin da wasu yankuna Nijar ke ciki sakamakon ambaliyar Ruwa
Halin da wasu yankuna Nijar ke ciki sakamakon ambaliyar Ruwa Laura Angela Bagnetto
Talla

A wani rahotan da Majalisar dinkin duniya ta fitar kan ambaliyar na cewa, gidajen sama da dubu 2 ne suka rushe yayin da gonaki sama da 540 ruwan ya wanke.

Majalisar dai ta nuna damuwar ta  kan wannan yanayi da ta ke gargadi cewa ka iya jefa al’ummar Nijar a cikin Fari saboda illar ruwan saman.

Rahotannin sun ce yanzu haka akwai mutane sama da dubu 3 da ke mafaka a makarantu da gidajen 'yan uwansu, ambaliyar dai ya fi tsananin a tsakiya da kuma yammacin kasar.

Tuni dai Gwamnatin Kasar ta bada sanarwa duk mutane da ke zaune a yankuna kusa da kogi su tashi saboda barazanar ambaliyar.

Cikin Jihohin 8 dake Jamhuriyar Niger, Jihar Diffa na gabashin kasar ne kawai amballiyar ba ta yiwa illa ba.

Ko a cikin shekarar ta 2014, irin wannan yanayi ya ta ba aukuwa a kasar, inda mutane da dama suka rasa rayukansu tare da kuma tursasawa dubai barin muhallinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.