Isa ga babban shafi
Nijar

Kaka ya lashe takobin kokuwar Nijar

Yahaya Kaka na Jihar Tawa  ya yi nasarar lashe takobi a kokuwar gargajiya ta bana da aka kammala a jihar Tawa karo na 38, bayan ya kayar da Lawali Dan Tela na  jihar Zinder a fafatawar karshe. 

Sabon sarkin takobin kokuwar gargajiya a Nijar, Yahya Kaka
Sabon sarkin takobin kokuwar gargajiya a Nijar, Yahya Kaka actunigernewspaper
Talla

Kaka da a yanzu ya zama sabon sarkin takobi, ya kayar da Dan Tela ne bayan mintina biyu da 'yan dakikoki da bude fage.

A karo na 10 kenan da jihar Tawa ke lashe takobi a tarihin kokuwar wadda a bana 'yan wasa 80 daga jihohi 8 na kasar suka kece raini.

Sabon sarkin na cikin sabbin  'yan wasan kokuwa da taurarinsu ke haskawa a wannan lokacin a Jamhuriyar Nijar, kuma jihar Tawa na alfahari da shi.

Daga cikin kyaututtukan da Yahya Kaka ya samu sun hada da miliyoyin kudi na CFA da kujerar makka da kuma filaye.

A tarihin kokuwar dai, jihar Maradi nada takubba 10, sai jihar Tawa da ita ma ta samu 10 a bana, yayin da  Zinder ke da  8, in da kuma jihar  Doso ke rike da 4, sai kuma  Niamey da Agadez da kowacce daga cikinsu ke da takubba 3.

Baki daga kasashe makwabta da suka hada da Najeriya na cikin mahalarta wannan kokuwar mai daukan hankula a Jamhuriyar Nijar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.