Isa ga babban shafi
Nepal

MDD ta damu game da jinkirin isar da kayan agaji a Nepal

Hukumar kula da lafiya al-umma ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwarta kan jan kafar da hukumar Kwastam ta Kasar ke yi dangane da isar da kayayyakin agaji ga wadanda bala’in girgizar Kasa ta shafa a Kasar Nepal

Jirgi mai saukan Ungulu ya isar da kayan agaji ga wasu daga cikin wadanda girgizar kasar ta shafa
Jirgi mai saukan Ungulu ya isar da kayan agaji ga wasu daga cikin wadanda girgizar kasar ta shafa REUTERS/Jitendra Prakash
Talla

Hukumar kula da lafiyar ta bukaci Firaministan Kasar ta Nepal, Sushil Koirala daya dau matakin shawo kan matsalar jinkirin isar da kayayyakin agajin.

Rahotannni sun bayyanna cewa, an jibge kayayyakin agaji da aka aiko daga kasashen ketere a wani karamin filin tashi da saukan jiragen sama na kasa da kasa dake birnin Kathmandu, yayin da kuma jami’an kwastam ke mayar da kayayyakin a kan iyakar kasar da India.

A ranar asabar din data gaba ta ne girgizar kasar ta auku kuma kawo an rasa rayukan mutane sama da dubu 6 baya wadanda suka rasa gidajeensu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.