Faransa
Kotun Faransa ta fara sauraren shari'ar matar da ta kashe 'ya'yanta
Wata Kotu a kasar Faransa ta fara sauraren shari’ar da ake yiwa wata mata da ta kashe 'ya'yanta guda 8 da zaran ta haife su.
Wallafawa ranar:
Talla
Matar mai suna Dominique Cottrez, mai shekaru 51 wadda tsohuwar ma’aikaciyar lafiya ce, ta amsa tambayoyi a kotun amma taki cewa komai game da mahaifinta wadda a baya tace shine uban 'ya'yan na ta.
Kotun ta saurari bayanin cewar matar kan shake jirajiran na ta ne har sai sun mutu da zaran ta haife su tsakanin shekarar 1989 zuwa shekara ta 2000.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu