Denmark da Sweden sun tsaurara tsaro a kan iyakokinsu
Kasar Denmark ta kaddamar da shirin gudanar da bincike akan iyakokin kasarta kan baki masu shiga kasar daga Jamus a wani yunkuri da ake ganin na iya haifar da matsala a kasashen Turai da ke anfani da fasfo din bai-daya da ake kira Schengen.
Wallafawa ranar:
Matakin na Denmark na zuwa ne sa’oi bayan kasar Sweden ta aiwatar da irin matakin wanda ya tilastawa baki da ke tafiya tsakanin kasashen biyu su nuna takardun shaida karo na farko a cikin shekaru 50.
Firaministan Denmark Lars Lokke Rasmussen yace ya dauki matakin ne don mayar da martani kan matakin da Sweden ta aiwatar.
Matakin dai zai shafi dubban ‘Yan gudun hijirar Syria da Iraqi da ke ci gaba da kwarara zuwa Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu