Jiragen yaki sun sake yin barin wuta a Aleppo
jiragen yaki sun yi luguden wuta a birnin Aleppo dake cigaba da kasancewa a hannun ‘yan tawaye Syria, tawagar likitoci dake aikin sa kai a kasar sunce harin ya shafi wani babban asibiti ba tare da yin karin bayani ba.
Wallafawa ranar:
Wannan dai shine karo na biyu da ake kai hari makamancin hakan a birnin na Aleppo a ‘yan kwanakin nan.
Rahotan Majalisar Dinkin Duniya na cewa mutane akalla dari hudu ne suka mutu a mako guda cikinsu har da yara kanana an kuma daura alhakin hare-haren akan dakarun Rasha dana bangaren gwamnatin shugaba Bashar Al-Assad.
Shekaru fiye da biyar kenan da barkewar yaki a Syria.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu