Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa ta kai kamfanin Lafarge kotu

Gwamnatin Faransa ta maka wani katafaren kamfanin kasar Lafarge a gaban kotu, kan laifin kin dakatar da aikin hakar siminti da ya yi a kasar Syria, duk kuwa da bukatar haramcin da kungiyar Tarayyar Turai ta yi.

Kamfanin Siminti na Lafarge
Kamfanin Siminti na Lafarge DRwikimedia
Talla

Ofishin ministan kudin Faransa ne, ya sanar da daukar wannan mataki na shigar da karar kamfanin a gaban wata kotun da ke birnin Paris.

Wata majiyar shari’a ta ce mai shigar da karar gwamnatin kasar ne, a cikin watan Oktoba ya buda soma binciken, dangane da zargin da ake yi wa katafaren kamfanin na Lafarge da ke aikin hakar simintin al’amarin da a yau ya kai shi ga shigar da karar a gaban kotu.

Ci gaba da gudanar da aikin da kamfanin hakar simintin ya yi a Jalabiya, a arewacin kasar Syria, karkashin wani reshen kamfanin na lafarge a yanki, ya haifar da kace nace a jaridar le Monde da ta bankado lamarin a watan Yunin bara, inda ta zargi kamfanin da ci gaba da gudanar da ayyukin hakar simintin a lokacin da ake cikin yaki a Syria, da cewa ya faru ne karkashin yarjejeniya da ya cimma da kungiyar mayakan jihadi ta IS a yankin.

Karar da ma’aikatar tattalin arzikin Faransa ta shigar dai, da ta shafi haramcin hana sayen man fetur din kasar ta Syria, da kungiyar Tarayyar Turai ta saka a 2012, karkashin jerin takunkuman da ta kakabawa gwamnatin shugaba Bachar Al-Assad.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.