Taron G20 ya karkata kan wadata rigakafin Covid 19 a duniya
Taron kasashe masu karfin tattalin arziki na G20, wanda Saudiya ke karbar bakuncinsa ya jaddada bukatar ganin an wadata duniya da allurar rigakafin cutar coronavirus.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugabannin kasashen G20 ciki har da Donald Trump na Amurka wanda ya ki amincewa da shan kaye a zaben shugaban kasar da ya gudana a farkon wannan wata sun bayyana a kwallaben talabijin a babban taron kafar intanet da ke gudana a yanayi na annobar coronavirus.
Taron na yini biyu ta kafar bidiyo wanda ke gudana tun a jiya Asabar, shine irinsa na farko da wata kasar Larabawa ke daukar nauyi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu