Isa ga babban shafi

Rasha ta fara girke makaman nukiliya masu cin gajeren zango a Belarus

Shugaban Belarus Alexander Lukashenko ya ce kasarsa ta fara karbar kananan makaman nukiliyar Rasha masu cin gajeren zango, wadanda ya ce karfin wasunsu ya ninka na nau’in bam din atomic da Amurka ta taba amfani da shi a kan Japan har sau uku.

Shugaban Belarus Alexander Lukashenko yayinjawabi ga manema labarai a yankin Minsk, dangane da makaman nukiliyar Rasha da suka fara karba. 13 ga Yuni, 2023.
Shugaban Belarus Alexander Lukashenko yayinjawabi ga manema labarai a yankin Minsk, dangane da makaman nukiliyar Rasha da suka fara karba. 13 ga Yuni, 2023. via REUTERS - PRESS SERVICE OF THE PRESIDENT O
Talla

Matakin dai shi ne irinsa na farko da Rasha ta dauka  tun bayan rugujewar Tarayyar Soviet.

A ranar Juma’ar da ta gabata shugaban Rasha Vladimir Putin ya bayyana cewar kasarsa, za ta ci gaba da sanya ido kan makaman nukiliyar da za ta fara jibge su a kasar Belarus, bayan shirya musu wuraren ajiya na musamman.

A watan Maris na kuma shugaban na Rasha ya bayyana cimma yarjejeniyar girke makaman a Belarus, inda ya alakanta daukar matakin da yadda Amurka ke tura n ata makaman nukiliyar masu cin gajeren zango, zuwa kasashen Turai cikin shekaru da dama da suka gabata.

Tuni dai Amurka ta caccaki matakin na Putin, duk da cewa ta bayar da tabbbacin cewa ba ta da aniyar sauya matsayinta kan manyan makaman nukiliya, kuma ba ta ga wasu alamun da ke nuna cewa Rasha na shirin yin amfani da na ta ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.