Isa ga babban shafi
Najeriya

Boko Haram ta kunshi kabilu da dama sabanin lokutan baya - Zulum

Gwamnan jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya, Babagana Umara-Zulum, ya ce a halin yanzu, mutane daga kabilun kasar da dama ne ke cikin kungiyar Boko Haram, sabanin kabila guda da a baya ake danganta su da kungiyar.

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum.
Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum. Pulse.ng
Talla

Gwamnan na Borno ya shaidawa manema labarai haka ne a wannan asabar, bayan ganawa da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a Abuja.

Umara Zulum ya kuma ce muddin ana son gaggauta kawo karshen matsalar Boko Haram, tilas dauki matakan warware matsalolin da suka haifar da tayarda kayar bayan, da kuma batutuwan da suke karfafa kungiyar ta Boko Haram.

Gwamnan ya kara da jaddada bukatar kara yawan jami’an tsaro a kauyukan dake jihar Borno, da kuma girke dakarun a inda babu su a baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.