Isa ga babban shafi
Benin

‘Yan takara 22 za su marawa Talon baya a zaben Benin

‘Yan takara 24 daga cikin 33 da suka tsaya zagayen farko na zaben shugabancin kasar Benin, sun kulla kawance domin marawa dan takarar adawa Patrice Talon a zagaye na biyu na zaben da za a yi a ranar Lahadi mai zuwa.

Allon yakin neman zaben Talon, a Cotonou
Allon yakin neman zaben Talon, a Cotonou REUTERS
Talla

Patrice Talon zai fafata ne da Firaministan Benin Lionel Zinsou a zagaye na biyu.

Wannan ne karon farko da aka samu kawancejam’iyyun adawa a Benin, domin marawa wani dan takara.

Daya daga cikin wadanda suka marawa Talon baya, tsohon Firaminista Pascal Irenee Koupaki, ya ce sun yi haka ne lura da cewa akwai manyan kalubale a gaban kasar Benin.

A cewar Mista Koupaki, lokaci ya yi da ya kamata al’ummar Benin su manta da bambancin da ke tsakaninsu, domin ta haka ne kawai za a iya ciyar kasa a gaba.

Bini Yayi dai zai sauka kan madafan ikon kasar bayan kammala wa’adin shugabanci biyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.