"Yan Sanda A Morocco Sun Dambace Da Masu Zanga-Zanga
Jami'an tsaro a kasar Morocco sun kara da masu zanga-zanga a yankin Al-Hoceima kwana daya bayan da Sarkin kasar Mohammed na shida ya soki jinkirin da ake samu na ayyukan ci gaba a yankin.
Wallafawa ranar:
Bayanai na nuna masu zanga-zangan sun tare hanyoyi yayin da ‘yan sanda suka yi kokarin fasa taron da karfin tsiya.
Majiyoyi na cewa masu boren sun fito ne daga garuruwan makwabta da suka hada da Imzouren da Tammassin.
Tun watan goma na shekarar data gabata ake samun yawaitan zanga-zanga a yankin Al-Hoceima mai tashan jiragen ruwa amma kuma ya kasance mafi koma baya ta fannin ci gaba a gunduman Rif.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu