Yan bindigar da suka sace dalibai mata a Kaduna, sun sake su
Rahotanni daga Najeriya sun ce yan bindigar da suka sace dalibai mata guda 6 a wata makarantar Sakandare dake Jihar Kaduna, sun sake su bayan karbar diyyar naira miliyan 10.
Wallafawa ranar:
Jaridar Premium Times da ake bugawaa Najeriya tace an saki daliban Makarantar ‘Engravers College’ ne yammacin jiya juma’a, inda daga bisani aka kai su ofishin yan Sanda da kuma asibiti domin duba lafiyar su.
Arewacin Najeriya ya kazanta da lamuran garkuwa da jama'a,a dai-dai lokacin da jama'a ke ci gaba da kokawa da rashin cikkaken tsaro a yankunan su.
Wasu daga cikin iyayen yaran da suka ga ‘yayan su sun tabbatar da labarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu