Isa ga babban shafi
Pakistan

Kungiyar ISIS ta kai hari ayarin motocin Mukaddashin Shugaban Majalisar Pakistan da Kashe mutane 27

Mayakan kungiyar IS masu ikirarin jihadi sun dauki alhakin wani kazamin hari na bam da aka kaiwa ayarin motocin mukaddashin shugaban majalisar Dattawan kasar Pakistan inda nan take aka kashe mutane 27.

Jamian tsaron Pakistan a harabar da aka tasar da wani Bam a birnin Parachinar a watan Janairu na wannan shekara.
Jamian tsaron Pakistan a harabar da aka tasar da wani Bam a birnin Parachinar a watan Janairu na wannan shekara. STR / AFP
Talla

Majiyoyin samun labarai na cewa wani dan kungiyar IS dauke da jigidan bama-bamai ne ya kai harin kusa da garin Mastung mai tazaran kilomita 50 da birnin Quetta.

Mukaddashin Shugaban majalisar Dattijan Abdul Ghafoor ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an so kashe shi ne, Allah bai nufa ba, duk da haka ya sami raunuka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.