Isa ga babban shafi
Masar

21 ga watan Afrilu za a yi Shari’ar Morsi a Masar

A ranar 21 ga watan Afrilu mai zuwa ne kotu a kasar Masar za ta yanke wa tsohon shugaban kasar Mohammad Morsi da kuma wasu magoya bayansa 14 da ake zargi da tunzura jama’a domin yin zanga-zanga hukunci.

Magoya bayan Muhammad Morsi a Masar
Magoya bayan Muhammad Morsi a Masar AFP PHOTO/OZAN KOSE
Talla

Hukuncin zai kasance na farko a jerin zarge-zargen da hukumomin kasar ke yi Morsi tun bayan da aka tunbuke shi daga karagar mulki cikin watan Yulin shekara ta 2013.

Za a yi Morsi shari’a ne tare da manyan shugabannin Jam’iyyar ‘Yan uwa Musulmi.

Kotun Masar na tuhumar Morsi da lafin cin amanar kasa musamman kan batun tserewar ‘yan gidan yari.

Tun hambarar da gwamnatin Morsi, an yanke wa daruruwan magoya bayansa hukuncin dauri da kisa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.