An bukaci Zuma ya bayyana sunayen masu sace kudin kasa
Jam’iyyun adawar kasar Afrika ta Kudu sun bukaci shugaba Jacob Zuma da ya gabatar da sunayen mutanen da ya ce ya sani suna sace kudin kasar.
Wallafawa ranar:
Wannan ya biyo bayan kalaman shugaban a Yankin Kwa Zulu Natal cewar ya san masu sace kudin kasar kuma yana kallon su.
Jam’iyyun adawa na DA da EFF ta Julius Malema sun ce ya zama wajibi ga shugaban ya mika sunayen mutanen ga ‘yan Sanda domin gudanar da aikin su akan wadanda ake zargin.
Shugaba Zuma ya dade yana tsallake rijiya da baya a kokarin tsige shi saboda zargin da ake masa na rub da ciki da kudaden talakawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu