ISIS na kara samun goyon baya a Somalia - UN
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwa kan yadda kungiyar IS ke cigaba da samun goyan baya a arewacin Somalia, inda ta ce rashin daukar mataki zai bai wa mayakan ISIS da suka gudu daga Iraq da Syria mafaka a yankin.
Wallafawa ranar:
Wani rahoto da majalisar ta fitar bayan harin sama da jiragen yakin Amurka suka kai, ya bayyana cewa yawan mayakan kungiyar da ke karkahsin Sheikh Abdulqader Mumin na cigaba da karuwa, kuma suna iya jefa daukacin yankin cikin tashin hankali.
Kasar Somalia ta fada cikin tashin hankali tun shekarar 1991 bayan kifar da gwamnatin shugaba Siad Bare.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu