Isa ga babban shafi
Nijar

Ana guje wa abincin kan hanya saboda kwalera a Nijar

A jamhuriyar Nijar, alkaluma na baya-bayan nan da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar na nuni da cewa adadin wadanda suka rasa rayukansu sakamakon cutar amai da gudawa wato Kwalara sun kai 67 a halin yanzu, kuma mafi yawansu a jihar Maradi. A jimilce mutane dubu 2 da 752 ne suka kamu da cutar a sassan kasar, in da a Maradi kawai aka samu asarar rayukan mutane 55. Tuni mutane suka yi ban kwana da cin abincin kan hanya saboda wannan annubar kamar yadda za ku ji a rahoton wakilinmu daga Maradi, Salissou Issa.

Cutar Kwalara ta kashe mutane 67 a Nijar
Cutar Kwalara ta kashe mutane 67 a Nijar REUTERS/Andreea Campeanu
Talla
01:31

Ana guje wa abincin kan hanya saboda kwalera a Nijar

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.