Ebola ta bulla a birnin Goma
Hukumomin Lafiya a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo sun sanar da cewa a karon farko an samu wanda ya kamu da cutar Ebola a Goma, birni na biyu mafi girma da ke kasar.
Wallafawa ranar:
Ma’aikatar lafiyar tace wani Fasto ne ya kamu da cutar, kuma ana kyautata zaton ya dauke ta ne daga mutanen da yake mu’amala da su a coci.
Rahotanni sun ce an fara ganin alamun cutar a jikin Faston ranar Talatar da ta gabata a garin Butembo, daya daga cikin garuruwan da suka yi fama da cutar, kafin ya koma Goma a motar safa.
Hukumomin sun ce yanzu haka ana kula da fasinjoji 18 da direbar motar da ya dauke shi daag Butembo zuwa Goma.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu