Isa ga babban shafi

Shugaban Saliyo Julius Maada Bio zai ziyarci unguwar da gobara ta tashi

Gwamnatin Saliyo tace adadin mutanen da suka mutu sakamakon gobarar da ta tashi a wani gidan mai ya kai 98, abinda yayi sanadiyar konewar motoci tare da mutanen da dake ciki.

Gobarar da ta tashi a wani gidan mai dake Freetown na kasar Saliyo
Gobarar da ta tashi a wani gidan mai dake Freetown na kasar Saliyo © afp.com - Saidu BAH
Talla

Hukumomin kula da lafiyar kasar sun ce  gawarwakin da suka tantance sakamakon hatsarin da ya faru a ranar juma’a sun kai 98, yayin da ake danganta hadarin da kama wutar da wata mota tayi sakamakon karo da motar dakon mai.

Unguwar da aka samu mutuwar mutane bayan gobarar da ta tashi a gidan mai a Saliyo
Unguwar da aka samu mutuwar mutane bayan gobarar da ta tashi a gidan mai a Saliyo via REUTERS - NATIONAL DISASTER MANAGEMENT AGE

Hukumar kai daukin gaggawa ta kasar ta bakin Shugaban ta tace zai yi wuya a tattance iyalan  mutanen da suka kone kurmus.

 Julius Maada Bio Shugaban kasar Saliyo
Julius Maada Bio Shugaban kasar Saliyo REUTERS/Olivia Acland

Fadar Shugaban kasar ta bayyana cewa shugaban kasa Julius Maada Biyo zai ziyarci unguwar da lamarin ya faru a yau lahadi biyo bayan bayyana kaduwar sa da hatsarin wanda ya kai ga asarar tarin rayuka .

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.