Isa ga babban shafi

An gudanar da jana'izzar Desmond Tutu a Afrika ta kudu

A yau asabar ,Afrika ta kudu ta gudanar da jana’izzar karshe ga jarumin kasar,mutumen da ya yaki tsarin nuna wariyar launin fata a kasar ,Desmond Tutu.

Jana'izzar  Desmond Tutu jagora a Afrika ta kudu
Jana'izzar Desmond Tutu jagora a Afrika ta kudu AFP - GIANLUIGI GUERCIA
Talla

A Afrika ta kudu,'Yan uwa ,abokanin arziki,jami’an gwamnati hata Shugaban kasar Cyril Ramaphosa ya halarci jana’aizzar a mujami’ar Anglicane ta Saint Georges inda aka gabatar da akwatin dake dauke da mammacin da ya rasu ranar 26 ga watan Disemba na shekarar da ta shude ya na mai shekaru 90 a Duniya.

Akwatin dake dauke da gawar Desmond Tutu
Akwatin dake dauke da gawar Desmond Tutu RODGER BOSCH AFP

Shugaban kasar yayinda yake gabatar da jawabin sa cikin jimami,ya bayyana mammacin a matsayin jarumi da sunan  sa ya zarce kan iyakokin Afrika ta kudu a gwagwarmayar da yayi tun wancan lokaci zuwa wannan.

jana'izzar Desmond Tutu a mujami'ar St Anglican dake Afrka ta kudu
jana'izzar Desmond Tutu a mujami'ar St Anglican dake Afrka ta kudu REUTERS - POOL

Ya kuma taka muhimiyar rawa tareda jarumai da suka hada da Nelson Mandela,Shugaban y ace ba za su iya mantawa da irin wadanan mutane.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.