Isa ga babban shafi

Wuta ta lakume ginin majalisar dokokin Afrika ta kudu

A Afrika ta Kudu, wata gobara ta tashi a majalisar dokokin kasar dake Cap Town,iftila’in da ya haddasa ruftawar rufin tsofuwar  majalisar kasar.

Gobara a majalisar dokokin Afrika ta kudu
Gobara a majalisar dokokin Afrika ta kudu AP - Tsvangirayo Mukwazhi
Talla

Ya zuwa yanzu,babu asarar rayuka,sai  dai wuta ta yadu zuwa  wasu gine-ginen majalisar da suka hada da gini sabuwar makjalisar dokokkin Afrika ta kudu.

Goabrar da ta tshi a majalisar dokokin Afrika ta kudu
Goabrar da ta tshi a majalisar dokokin Afrika ta kudu AFP - OBED ZILWA

Jean Pierre Smith memba ne a da’irar magajin garin Cape Town,ya sheidawa manema labarai cewa duk da ruftawar rufin tsofuwar majalisar dokkokin kasar,jami’an kwana-kwana na iya kokarin ceto abinda ya saura daga kayakin tarihi  musaman littatafan dake ajiye a zauren tsofuwar majalisar dokkokin .

Shugaban kasar Cyril Ramaphosa da ya isa wurin ya sheidawa manema labarai cewa ,yan sanda na tsare da mutun daya yanzu haka,kuma bincike na tafiya a kai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.