Mun kusa kawo karshen zazzabin cizon sauro a Afirka - UNICEF
Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, tare da kungiyar lafiya ta Gavi, sun fitar da sanarwar cewa nan ba da jimawa ba, za a kawo karshen cutar zazzabin cizon sauraro, musamman a wasu kasashen Afirka da cutar tafi kamari, ta hanyar rarraba alluran rigakafin wannan cuta da ke yiwa kananan yara kisan mummuke.
Wallafawa ranar:
Wannan na zuwa ne, bayan jirgin farko dauke da dubban alluran wannan rigakafi da ya sauka a Jamhuriyar Kamaru, bayan da aka gudanar da gwaje-gwajen rigakafin cutar a kasashen Kenya, Ghana da Malawi, har ma aka samu nasarar rage adadin masu kamuwa da ita fiye da yanda aka tsammata.
Hukumomin lafiyar biyu sun bayyana wannan ci gaba na allura da aka samu a matsayin, musamman wajen kawar da daya daga cikin cutuka mafiya hatsari da ke barazana ga kananan yara a nahiyar Afirka.
Karin asu alluran rigakafin da adadin su ya haura miliyan daya da dubu dari bakwai, nan ba da jimawa ba UNICEF ya ce za a aika su kasashen Burkina Fasio, Laberiya, Niger da kuma Saliyo.
Shugaban UNICEf, Catherine Russell, gabatar da wannan shiri na rigakafi, sjhakka babu zai kawo karshen fargabar da iyaye da kuma hukumomin lafiya ke ciki, game da illar da wannan cuta ke haifarwa a kasashe, musamman masu raunin tattalin arziki.
Kasashen Afirka da dama na shirye-shiryen yadda za su sanya alluran rigakafin zazzabin cizon sauro cikin rukunan rigakafin da ake yiwa yawa, inda ake sa ran za su fara amfani da wannan shiri daga Watan Janairu zuwa Maris din shekarar badi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu