Isa ga babban shafi
Syria-Turkiya

Fiye da farar hula dubu 200 sun tsere daga Syria cikin wata guda-MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce jumullar fararen hula dubu dari biyu da 35 ne suka tsere daga yankin Idlib a cikin makwanni biyu da suka wuce, yayin da gwamnatin Syria da Rasha suka zafafa luguden wuta da su ke yi akan tungar karshe na ‘yan tawaye.

Fararen hula akan hanyarsu ta barin Syria.
Fararen hula akan hanyarsu ta barin Syria. Delil SOULEIMAN / AFP
Talla

Hukumar kula da aiki jinkai ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce wannan mummunar al’amari da ya auko a tsakanin 12 da 25 ga watan Disamba ya kusan mayar da garin Maaret al-Numan kufai .

Wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa a yankin ya ce ya ga mutane da dama na barin garin a cikin jerin gwano.

Motocin akori kura ne ke ta zirga-zirga a babbar hanyar da ta hade kudancin yankin Idlib da arewacin Syria, inda suke ta jigilar fararen hula zuwa tudun mun tsira.

Tun a tsakiyar watan Disamba dakarun Syria da ke samun goyon bayan Rasha suka shiga diran mikiya kan mujahidai a yankin Idlib, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka yi a watan Agusta, da kuma kiraye-kirayen da Turkiya, Faransa da Majalisar Dinkin Duniya ke ta yi na a kwantar da hankula.

Mujahidan kungiyar Hayat Tahrir al- Sham da ke da alaka a da, da kungiyar al - Qaeda ne suka fi rinjaye a yankin Idlib, inda ma shugabansu ya yi kira ga ‘yan kungyar da su yi fito na fito da masu mamaya daga Rasha.

‘Yan gudun hijira akalla miliyan 3 ne ke wannan yankin na Idlib, sakamakon shekaru da aka kwashe ana gwabza fada a wasu sassan Syria. Yakin Syria ya kashe sama da mutane dubu 370, ya kuma daidaita miliyoyi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.