Isa ga babban shafi

China ta goyi bayan Rasha kan matakinta na kin janyewa daga yakin Ukraine

China ta marawa Rasha baya kan kudirinta na kin janyewa daga yakin da ta ke yi a Ukraine kamar yadda wata sanarwar taron ministocin kasashe 20 mafiya karfin tattalin arziki na G20 da ke gudana a birnin New Delhi na india ta sanar. 

Wata ganwar shugaba Vladimir Putin da takwaransa Xi Jinping na China.
Wata ganwar shugaba Vladimir Putin da takwaransa Xi Jinping na China. AP - Mikhail Klimentyev
Talla

China da Rasha, su kadai ne daga cikin mambobin kasashen G20 suka ki amincewa da sanarwar da ke bukatar Rasha da ta  janye baki daya kuma nan take daga kasar Ukraine. 

Ministan Harkokin Wajen China, Qin Gang ya ce, za su ci gaba da zantawa da Rasha da kuma ba ta hadin-kai a dukkanin matakai a yayin taron na G20. 

Ko da ya ke Mista Gang ya ce, ya shaida wa takwaransa na Rasha Sergey Lavrov cewa, suna goyon bayan Moscow dari bisa dari kan shiga tattaunawar zaman lafiya kuma Chinar a shirye ta ke ta taka rawa a wannan fannin a cewarsa. 

Akasarin mambobin kasashen G20 sun yi tir da yakin da ake yi a Ukraine, in ban da Rasha da China da suka nuna ko-oho. 

Kasashen yammaci dai na cike da fargaba kan yiwuwar Chinan ta fara taimakawa Rasha da makamai, batun da ke cikin abubuwan da za a tattauna a taron na G20.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.