Isa ga babban shafi

Wakilan kasashen Yamma na taro kan yadda za a ceto kasar Haiti

Wakilai daga manyan kasashen duniya za su gana a yau litinin a yankin Karebiya, domin tunkarar halin da ake ciki a kasar Haiti, yayin da tashe-tashen hankulan kungiyoyin ‘yan daba suka gurgunta babban birnin kasar da ke fama da talauci tare da tilastawa jami'an diflomasiyyar kasashen waje tserewa a karshen mako.

Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken kenan kan hanyarsa ta zzuwa Jamaica diomin halartar taron gaggawa da kasashen yankin Karebiya suka shirya game da makomar Haiti da ke hannun kungiyoyin 'yan daba a halin yanzu.
Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken kenan kan hanyarsa ta zzuwa Jamaica diomin halartar taron gaggawa da kasashen yankin Karebiya suka shirya game da makomar Haiti da ke hannun kungiyoyin 'yan daba a halin yanzu. AFP - ANDREW CABALLERO-REYNOLDS
Talla

Kungiyoyin ‘yan daba, wadanda tuni suka karbe ikon mafi yawan yankunan Port-au-Prince da kuma hanyoyin da suka bi zuwa sauran sassan kasar, sun yi barna a cikin 'yan kwanakin nan, yayin da suke kokarin hambarar da Firaminista Ariel Henry a matsayin shugaban kasa mafi talauci a Yammacin Duniya.

Kawancen kasashen yankin Karebiya CARICOM, ya gayyaci jakadu daga kasashen Amurka, Faransa, Canada da kuma Majalisar Dinkin Duniya zuwa wani taro a kasar Jamaica domin tattauna tashe-tashen hankula da kuma za a ceto kasar ta Haiti.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, mataimakin shugaban kasar Guyana, Bharrat Jagdeo, ya ce kasashen za su nemi samar da tsaro tare da cire shakku ga al'ummar Haiti.

Yayin da lamura ke kara tabarbarewa, an gano yadda gawarwaki ke kwance a titunan Port-au-Prince inda hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta MDD ta ce wannan tashin hankalin ya raba al’ummar Haiti 362,000 da muhallansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.