Isa ga babban shafi
Rasha-Ukraine

‘Yan kishin Rasha suna nan kan bakarsu

‘Yan tsagera a kasar Ukraine sun bayyana aniyarsu na ci gaba da shirin gudanar da zaben raba gardama domin neman ‘yancin kai a gabacin kasar, suna masu yin watsi da kiran shugaban kasar Rasha Vladimir Putin akan su dage gudanar da zaben.

Masu Zanga-zanga dauke da Tutar sabuwar kasar Jamhuriyyar Donetsk da suke shirin jefa kuri'ar ballewa daga Ukraine a harabar Ofishin Jekadancin Jamus a Riga
Masu Zanga-zanga dauke da Tutar sabuwar kasar Jamhuriyyar Donetsk da suke shirin jefa kuri'ar ballewa daga Ukraine a harabar Ofishin Jekadancin Jamus a Riga REUTERS/Ints Kalnins
Talla

A ranar Lahadi ne ‘Yan tawayen suka shirya gudanar da zaben raba gardama domin kafa kasar Jamhuriyyar Donetsk.

Akwai fargabar yiyuwar ballewar rikici a Ukraine a yayin da Rasha da kasashen Tsohuwar daular Soviet ke bikin samun galaba akan Dakarun Jamus a yakin duniya na biyu.

Ana sa ran Shugaban Rasha Putin zai kai ziyara yankin Crimea da ya balle daga Ukraine a watan Maris a daidai lokacin da dakarun Rasha suka gudanar da atisaye a kan iyaka da Ukraine.

Kasashen Amurka da Turai sun yi barazanar sake kakabawa Rasha takunkumi idan har masu ra’ayinta a Ukraine suka jefa kuri’ar amincewa su balle daga Ukraine.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.