MDD ta nemi a mutunta tsagaita wuta a kasar Ukraine
Majalisar Dinkin Duniya ta nemi bangarorin da ke rikici da juna a kasar Ukraine su mutunta yarjejeniyar tsagaita wutan dake ci gaba da tangal tangal, a daidai lokacin da suke zargin juna da haddasa rikicin. Lokacin da yake jawabi, yayin da kungiyar taraiyyar Turai ta EU ke shirin kakakba wa Rasha karin takunkumi kan rawar da ake zargi tana takawa a rikicin na Ukraine, jami’i mai kula da harkokin siyasa na Majalisar ta Dinkin Duniya Jeffrey Feltman, yayi gargadin cewa yarjejeniyan zaman lafiyan kasar na cikin hadari.Ana shirin tsawaita takunkumin tattalin arzikin da aka sanya wa Rasha zuwa watanni 6 masu zuwa, lamarin da zai shafi harkokin bankin da hada hadar man kasar.
Wallafawa ranar: