Majalisar Tsarin Mulkin Faransa ta amince da dokar tilasta yin rigakafin Korona
Majalisar Tsarin Mulkin Faransa ta amince da sabuwar dokar rigakafin Korona, wadda ta tilastawa mutane masu shekaru 16 zuwa sama nuna shaidar yin allurar rigakafin cutar, kafin shiga wuraren taron jama'a kamar mashaya, gidajen abinci da gidajen Sinima.
Wallafawa ranar:
Sabuwar dokar dakile yaduwar annobar ta Korona dai, wani bangare ne na yunkurin shugaba Emmanuel Macron da ya sha alwashin kuntatawa tsirarun mutanen da ba a yi musu allurar rigakafin cutar Koronar ba.
Dokar tilasta nuna shaidar rigakafin Koronar dai, za ta fara aiki ne daga ranar 24 ga Janairu, wadda ta maye gurbin dokar nuna takardar shaidar rigakafin, ko gwajin mutum ba ya dauke da cutar, ko kuma shaidar da ke nuna warkewa daga cutar.
Sai dai Majalisar tsarin mulkin kasar ta Faransa, ta ki amincewa da bukatar gwamnati ta tilastawa masu halartar tarukan Siyasa nuna shaidar karbar rigakafin na Korona.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu