Yan Boko Haram sun kashe sojan Najeriya
Mayakan boko Haram sun kashe akalla sojin Najeriya guda lokacin da suka yiwa tawagar dakarun kwantan bauna a kauyen Kamuya dake Jihar Barno dake arewacin kasar.
Wallafawa ranar:
Wata majiyar soji ta shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewar, yan bindigar sun kai harin ne da misalin karfe 11.30 na rana, inda suka kashe soja guda da raunana wasu guda 3.
Kauyen Kamuya da mahaifiyar shugaban sojin Najeriya Janar Tukur Buratai ta fito, ya dade yana gamuwa da hare haren mayakan boko haram.
Gwamnatin Najeriya a dai-dai lokacin da kungiyar Boko Haram ke cika shekaru goma,hukumomin kasar na ci gaba da neman hanyoyin kawo karshen rikicin da ya lakume rayuka da dama a Najeriya dama wajen kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu