Nijar
Yan Boko Haram sun kaiwa sojojin Nijar Hari a Jihar Diffa
Wasu da ake zargin cewa magoya bayan kungiyar Boko Haram ne, sun kashe jami’an tsaron jamhuriyar Nijar 6 tare da raunata wasu uku a wani wuri mai tazarar kilomita 20 daga garin Diffa.
Wallafawa ranar:
Talla
Sanarwar da ma’aikatar cikin gidan kasar ta fitar ta ce ‘yan Boko Haram sun yi wa sojojin kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri a yankin na Diffa dake kusa da iyaka da tarayyar Najeriya.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar na kokarin gani ta kawo karshen ta’adanci a yankin Diffa dake iyaka da kasashen Cadi da Najeriya a cewar ma’aikatar cikin gidan Jamhuriyar Nijar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu