Isa ga babban shafi
Najeriya

Kungiyar Boko Haram ta sako wasu daga cikin yan matan Chibok

Rahotanni Daga Najeriya sun ce kungiyar Boko Haram ta saki Yan Matan Chibok da dama da ta sace sama da shekaru biyu sakamakon tattaunawar da suka yi da gwamnati.

'Yan matan makarantar Chibok da Boko Haram suka yi garkuwa da su
'Yan matan makarantar Chibok da Boko Haram suka yi garkuwa da su
Talla

Ya zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance dake tabbatar da adadin Yan Matan da aka sake, amma kafofin yada labarai da dama sun jiyo daga jami’an tsaro cewar adadin ya kai 80, kuma yanzu haka Yan Matan na Banki dake kusa da iyakar Kamaru.

Ana saran Gwamnatin Najeriya tayi Karin haske akai nan gaba kadan.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.