Isa ga babban shafi
Afrika ta tsakiya

MDD ta kara dakarun wanzar da zaman lafiya a CAR

Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da karin dakaru 900 domin karfafa rundunar wanzar da zaman lafiya da tsaro a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Wasu daga cikin dakarun Minusca a babban birnin Bangui na Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya
Wasu daga cikin dakarun Minusca a babban birnin Bangui na Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya AFP PHOTO / STRINGER
Talla

Kara adadin dakarun wanzar da zaman lafiyar ta Minusca na daga cikin alkawurran da babban magatakarda na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya dauka lokacin da ya ziyarci kasar a cikin watan jiya.

Har ila yau Kwamitin Tsaron ya amince da tsawaita wa’adin aikin rundunar da ke kokarin wanzar da tsaro da zaman lafiya a kasar mai fama da yakin basasa tun a shekara ta 2013.

Kafin wannan kari dai, akwai dakaru dubu 11 da 650 da suka hada da ‘yan sanda dubu biyu da 80 da ke aiki a karkashin rundunar ta Minusca, to sai dai ko baya ga gazawa ta fannin samar wa fararen hula tsaro, hatta su kansu dakarun na fuskantar hare-hare daga ‘yan bindiga.

Sai dai kara adadin dakarun na zuwa ne a daidai lokacin da Amurka ta fara aiwatar da siyasarta ta rage kudaden da take kashewa domin tallafa wa ayyukan wanzar da zaman lafiya a sassan duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.