Isa ga babban shafi

Kagame na Rwanda ya yiwa manyan sojojin kasar 83 ritayar dole

Sa’o’i kalilan bayan juyin mulkin soji a Gabon, shugaba Paul Kagame ya sanar da garambawul ga Ma’aikatar Tsaron Kasar wanda ya kai ga tilasta ritaya ga wasu manyan jami’ai.

Shugaba Paul Kagame na Rwanda.
Shugaba Paul Kagame na Rwanda. REUTERS - JEAN BIZIMANA
Talla

Sanarwar da rundunar tsaron Rwanda ta wallafa a shafinta na X da aka fi sani da Twitter ta ce, ritayar dolen ta shafi manyan jami’an soji 83.

Sanarwar ta ce, tuni shugaban ya sahale karin girma ga wasu kananan jami’ai don maye gurbin wadanda aka yi wa ritayar dolen.

Shugaba Paul Kagame mai shekaru 65 da ya hau mulkin kasar tun a shekarar 2000, a shekarar 2015 ya yi wani gyaran fuska ga kundin tsarin mulkin kasar da ya sahale masa ci gaba da mulki har zuwa shekarar 2034.

Wannan mataki na shugaba Kagame na zuwa ne kwana guda bayan juyin mulkin da sojoji suka jagoranta a Gabon da ya kawo karshen mulkin tsawon shekaru 53 da iyalan gidan Bongo suka shafe suna yi a kasar mai arzikin man fetur.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.