ICPC: Osinbanjo ya janye sunan mutanen da ake zargi da Rashawa
Mukaddashin Shugaban Najeriya Yemi Osinbanjo ya janye suna wasu mutane biyu da aka nada a hukumar gudanarwar hukumar yaki da almundahana ta ICPC saboda zargin da ake musu na cin hanci da rashawa.
Wallafawa ranar:
Mai taimakawa shugaban Laolu Akande ya ce an janye sunan Maimuna Aliyu da Sa’ad Alanamu daga cikin sunayen da Osibanjo ya bayyana a matsayin hukumar gudanarwar.
Ana tuhumnar Alanamu ne kan zargin cin hanci lokacin da ya rike mukamin shugaban hukumar kula da ilimi mai zurfi a Kwara, yayin da ita kuma Maimuna Aliyu ake zargin ta karya ka’idar aiki da karkata kudaden talakawa lokacin da take aiki a asusun ajiyar Aso Savings.
Nadin mutanen biyu ya gamu da suka daga sassan Najeriya saboda tuhumar da ake musu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu