Isa ga babban shafi
Najeriya

Ganduje ya bukaci Fulani su koma Kano da kiwo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci daukacin Fulani makiyaya da ke sassan Najeriya musamma a jihohin Benue da Taraba da su koma Kano don ci gaba da kiwon dabbobinsu.

Ana yawan alakanta wasu hare-hare a sassa Najeriya da Fulani makiyaya, zargin da kungiyar Miyetti-Allah ta Fulani ta sha musantawa
Ana yawan alakanta wasu hare-hare a sassa Najeriya da Fulani makiyaya, zargin da kungiyar Miyetti-Allah ta Fulani ta sha musantawa guardian.ng
Talla

Gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje ya ce, jiharsa na da manyan filayen kiwo da za su karbi makiyayan da dabbobinsu.

Ganduje ya bayyana haka ne a yayin sanya ido a shirin rigakafin cutukan dabbobi musamman shanu sama da miliyan 1 a karamar hukumar Garum Malam da ke jihar.

Ganduje ya kuma yi Allah Wadai da rikicin Fulani makiyaya da manoma na baya-bayan da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama a sassan kasar, in da ya ce, dole ne a kawo karshen kisan da ake danganta wa Fulani

Daga cikin wuraren da Ganduje ya ce za su karbi Fulanin da ya gayyata, sun hada da Gaya da Rogo da Kura da Tudun Wada da Ungoggo, in da ake da manyan filayen noma da kiwo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.