Isa ga babban shafi
Wasanni

Chelsea za ta kai matakin gaba a gasar Turai- Hiddink

Kocin Chelsea, Guus Hiddink ya yi amanna cewa, kungiyarsa na da damar kai wa matakin wasan dab da na kusan karshe a gasar cin kofin zakarun Turai kamar yadda PSG ke da irin wannan damar, duk da cewa PSG din ta doke ta da ci 2-1 a jiya talata.

Kocin Chelsea Guus Hiddink
Kocin Chelsea Guus Hiddink Reuters/Andrew Boyers
Talla

A karawarsu ta jiya,  PSG ce ta fara zura kwallo  ta hannu Zlatan Ibrahimovic a minti na 39 amma daga bisani Mikel Obi na Chelsea ya barke kwallon a minti na 45.

To sai kuma, Edison Cavani na PSG ya samu nasarar zura kwallo guda, lamarin da ya bai wa PSG damar doke Chelsea da ci 2-1.

A karo na biyu kenan da Mikel Obi, dan asalin kasar Najeriya ya ci wa Chelsea kwallo a gasar zakarun Turai, amma a jumulce, sau shida kenan cikin kusan shekara 10 da ya ciwa Chelsea din kwallo.

Sannan a karon farko kenan da Chelsea ta yi rashin nasara tun bayan da ta nada Guus Hiddink a matsayin sabon kocinta bayan ta kori Jose Mourinho a watan Disamban bara.

A ranar 9 ga watan Maris mai zuwa kungiyoyin biyu za su sake kece raini a filin wasa na Stamford Bridge.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.