Mahrez ne gwarzon Afrika
Riyad Mahrez ne na Algeria ya lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na Afrika bayan ya samu kuri’u fiye da dan kasar Gabon Pierre-Emerick Aubameyang da ya lashe kyautar a bara.
Wallafawa ranar:
Mahrez dai ya taka rawar gani ga nasarar da Leicester City ta samu na lashe kofin Firimiya inda kuma ya jefa kwallaye 17.
Pierre-Emerick Aubameyang na Borussia Dortmund ne ya zo a matsayi na biyu sai Dan wasan Liverpool Sadio Mane na Senegal ya zo a matsayi na uku a bikin da aka gudanar a birnin Abuja na Najeriya
A bangaren mata ‘yar kwallon Najeriya da ke wasa a Arsenal Asisat Oshoala ceta lashe kyautar, kuma karo na biyu ke nan tana lashe kyautar bayan ta karba a 2014.
Kungiyar Super Falcons na Najeeiya ne aka ba kyautar babbar kungiya a Afrika, bayan lashe kofin afrika na Mata a kamaru a bana. A bangaren Maza Uganda ce ta karbi kyautar.
Kwalkifan Memolodi Sundown da ta lashe kofin Zakarun Afrika aka ba gwarzon dan wasan Afrika da ke taka kwallo a gida.
‘Yan wasan Najeriya Kelechi Iheanacho na Manchester City da Alex Iwobi na Arsenal ne suka lashe kyautar gwarzaye masu tasowa.
Bakary Papa Gassama ne ya lashe kyautar gwarzon alkalin wasa a karo na uku a jere da jere
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu