Isa ga babban shafi
Uganda

Wata cuta mai kama da Ebola ta kashe mutane a Uganda

Wata cuta mai kama da Ebola da masana kiwon lafiya ke kira Marburg, ta yi sanadiyyar mutuwar mutum biyu a Uganda.

Wata cuta mai kama da Ebola na kisa a Uganda
Wata cuta mai kama da Ebola na kisa a Uganda Tyler Hicks/Liaison
Talla

Ma’aikatar kiwon lafiyar kasar ta ce bayan gwaje-gwajen da aka gudanar a kan gawarwakin mutanen biyu da suka mutu, an tabbatar da cewa cutar ce wadda ke haddasa tsiyayar jini a cikin jikin dan adam ta yi sanadiyyar ajalinsu.

Cibiyar binciken cututtuka masu yaduwa a kasar, ta ce cutar da ake kira Marburg ta soma bula ne a kasar cikin wani yankin da ake kira Kamwenge a shekara ta 2007.

Cutar da ke yaduwa kamar Ebola, a shekara ta 2012 ta yi sanadi rai 10, kazalika a 2014 ta kashe mutun guda.

Marburg sunan wani yankin ne na Jamus, inda aka fara samun bular cutar a shekara ta 1967.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.