'Yan sandan Gabon sun kame mutane da dama a Libreville
Jami’an ‘yan sanda a birnin Libreville na kasar Gabon, sun cafke mutane da dama mafi yawansu ‘yan asalin kasashen yammacin Afirika, bayan da wani da aka ce dan Nijar ne, ya daba wa wasu ma’aikatan talabijin na tashar National Geographic ‘yan kasar Danemark wuka.
Wallafawa ranar:
Duk da cewa ba a bayyana sunan maharin ba, an bayyana cewa shekarunsu 59 ne kuma ya share akalla shekaru 19 zaune a kasar ta Gabon.
Mafi akasarin wadanda aka kame, bayan samamen da jami'an tsaron suka kai kan wata kasuwa a Libraville, Hausawa ne da suka shafe tsawon lokaci suna hada-hada.
A ranar Asabar mutumin ya kai wa wasu ‘yan kasar Denmark hari da wuka yana kabbara, sai dai rundunar 'yan sandan kasar ta zargi wadanda suka shaida kai harin da yunkurin hana sanar da ita halin da ake ciki, matakin da ta ce ta dauke shi a matsayin goyon baya ga aikata ta'addanci.
Rundunar ‘yan sandan Gabon ta ce, mutumin ya shaida mata cewa ya kai harin ne don maidawa Amurka Martani, bisa goyon bayan mai da birnin Kudus babban birnin kasar Isra’ila.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu