Shugaban Hukumar CAF ya kamu da coronavirus
Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Afirka, CAF, Ahmad Ahmad, ya kamu da annobar COVID-19.
Wallafawa ranar:
Labarin na kunshe ne a cikin wata sanarwa a shafin intanet na hukumar kwallon kafar nahiyar .
Sanarwar ta ce, Ahmad ya nuna almun cutar ne, bayan isar Alkahiran Masar a ranar 28 ga watan nan na Oktoba, abin da yasa akayi masa gwaji, kuma aka tabbatar ya kamu da cutar, kuma yanzu haka ya killace kansa a wani Otel na tsawon kwanki 14.
Wannan na zuwa ne kwanaki kalilan bayan da shugaban ya nuna aniyar sake neman wa'adi na biyu a jagorancin Hukumar Kwallon Kafar Afirka, bayan da kasar sa Madagascar ta amince ya ci gaba da wakilcin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu