Isa ga babban shafi
KISAN-KIYASHI

An kammala shara’ar aikata laifin kisan kiyashin ga wasu yan kasar Rwanda biyu a Belgium

Hotunan wasu daga cikin  yan kabilar Tutsi, da aka yi wa kisan kare dangi   Rwanda a 1994, da aka kafa a cibiyar tattara tarihin kisan kare dangin kasar a Kigali,  5 avril 2019.
Hotunan wasu daga cikin yan kabilar Tutsi, da aka yi wa kisan kare dangi Rwanda a 1994, da aka kafa a cibiyar tattara tarihin kisan kare dangin kasar a Kigali, 5 avril 2019. AP - Ben Curtis
Talla

An kawo karshen shara’ar kisan kiyashin da ake yi wa wasu yan kasar Rwanda biyu a kotun Bruxelles na kasar Belgium.

A cikin daren ranakun  alhamis zuwa safiyar juma’a ne, kotun ta yanke wa  Séraphin Twahirwa, dan shekaru 66 hukumcin daurin rai da rai.  Tare  da bada umarnin daure  Pierre Basabose, mai shekaru 76 a duniya,  duk da cewa, ya na fama da matsalar tabin hankali,  da kuma tsufa  kamar yadda likitoci suka sanar.

A ranar talatar da ta gabata ne, kotun ta bayyana mutanen biyu a matsayin wadanda suka aikata  laifin kisan kiyashi da laifukan yakin da aka aikata a tsakanin watan avrilu zuwa yunin 1994 a kasar Rwanda

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.