Isa ga babban shafi

Kasashe 45 ne ke tsananin bukatar taimakon abinci daga ketare-MDD

Hukumar samar da  abinci ta majalisar dinkin duniya tace kasashen Africa 33 ne ke tsananin bukatar abinci daga kasashen ketare ko kuma hukumomin bada agaji na duniya.

Karancin abinci na ci gaba da galabaitar da jama'a a Nahiyar Afrika
Karancin abinci na ci gaba da galabaitar da jama'a a Nahiyar Afrika © GUERCHOM NDEBO / AFP
Talla

Hukumar ta FAO ta ce jimilla kasashen duniya 45 ke da wannan bukata cikin gaggawa cikin su 33 daga nahiyar Africa, sai 9 daga yankin Asia da guda 2 daga yankin Latin Amurka da Karebiya sai guda1 a yankin turai.

Rahoton da hukumar ta fitar yace wannan bukata ta samo asali ne sakamakon tashin hankali da ake fama da shi a yankin gabashin Asia, da kuma yammaci da gabashin Africa, lamarin da ke ta’azzara karancin abinci.

Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da ake samun karuwar kwararar hamada a wasu kasashen kudancin Africa.

Rahoton ya ci gaba da cewa noma da fitar da alkama ya ragu matuka a Afrika ta kudu, kasar da ke kan gaba wajen fitar da alkamar a nahiyar Afrika, a sakamakon tsananin zafi da sauyin yanayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.