Sudan-Sudan ta Kudu
Sudan ta Kudu ta zargi Sudan da kai ma ta hari
Sudan ta kudu ta zargi kasar Sudan da kai harin sama kan Yankunan da suke takaddama a akai kafin gudanar da taron shugabanin kasashen biyu da za’a yi dan kawo karshen tankiyar da ake samu a tsakaninsu. Ministan yada labaran kasar, Barnaba Marial Benjamin, yace fararen hula da dama sun samu raunuka a hare haren.
Wallafawa ranar:
Talla
Kasashen biyu dai sun dade sun rikici a tsakaninsu kan Yankin Abyei mai arzikin man fetur. Daga Khartoum wakilin RFI Hausa Mannir Sani Furagirke ya yi Karin bayani game da wannan batu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu