Isa ga babban shafi

Amurka ta bukaci korar Rasha daga zama wakiliya a Hukumar kare Hakkin Bil Adama

Sakataren harakokin wajen Amurka Antony Blinken ya bukaci korar Rasha daga zama wakiliya a Hukumar kare Hakkin Bil Adama ta Majalisar Dinkin Duniya saboda mamayar da ta yiwa Ukraine.

Shugaban Rasha  Vladimir Poutine
Shugaban Rasha Vladimir Poutine AP - Mikhail Metzel
Talla

Yayin da yake jawabi ga zaman Majalisar ta bidiyo, Blinken yace bai ga dalilin da kasar da ta mamaye wata kasa ta kuma aikata munanan laifuffukankare hakkin Bil Adama zata zauna a cikin majalisar ba.

 Antony Blinken Sakataren harakokin wajen Amurka
Antony Blinken Sakataren harakokin wajen Amurka © 2019 AFP

Lokacin gudanar da wannan taro, jakadun kasashen duniya sun fice daga zauren taron lokacin da Sakataren harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov ya fara jawabin sa.

MInistan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov tare da takwaransa na Rasha Peter Szijjarto.
MInistan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov tare da takwaransa na Rasha Peter Szijjarto. REUTERS - Sergei Karpukhin

Majalisar ta bayyana matukar damuwa dangane da mamaye Ukraine da Rasha tayi, wanda ya haifar da rasa dimbin rayuka da kuma tilastawa akalla mutane miliyan guda barin gidajen su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.