Isa ga babban shafi

Majalisar Dinkin Duniya na nazari game da tsaftataccen ruwan sha a Duniya

22 ga watan Marisce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin nazari game da tsaftataccen  ruwan sha a sassan Duniya.Bikin na bana na zuwa ne a dai dai lokacin da ake fuskantar matsalar ruwan sakamakon karancin wutar lantarki da kuma na man fetur a Najeriya, lamarin da ya sanya wasu ‘yan garuwa gudanar da yajin aiki a wani bangare a jahar Lagos.

Matsallar ruwan sha zata shafi mutane milyan biyar
Matsallar ruwan sha zata shafi mutane milyan biyar © Pixabay
Talla

A yan kwanakin nan karancin wutar lantarki a Najeriya ya ta’azzara matsalar karancin ruwa, lamarin da ya sa ‘yan garuwa a unguwar Idi-araba da ke birnin Lagos suka gudanar da yajin aiki kamar yadda wani magidanci Malam Habu ya tabbatar.

A Kampala,jama'a na bukatar ruwan sha
A Kampala,jama'a na bukatar ruwan sha Photothek via Getty Images - Ute Grabowsky

Asusun tallafawa ilimi, kimiyya da raya al’adu na majalisar dinkin duniya UNESCO ne ke wadannan kalamai, a wani bangare na bukukuwan Ranar ruwa ta duniya da ake gudanarwa duk ranar 22 ga watan Maris din kowacce shekara. 

wani kauye a kasar Chadi inda jama'a ke bukatar ruwan sha
wani kauye a kasar Chadi inda jama'a ke bukatar ruwan sha © RFI / Sayouba Traoré

Ta cikin wani rahoto da ausun ta fitar, ta ce kaso 99 na dukannin narkakken abu dake karkashin kasa, ruwa ne, duk da cewa akwai karancin wannan ilimi a tsakanin al’ummar duniya.

Khamis Saleh ya kewaya birnin Lagos don gane wa idanunsa halin da ake ciki, ga kuma rahotonsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.