Isa ga babban shafi

Majalisar sojin Burkina Faso na shirin ganawa da yan kasar a gobe

Majalisar sojin Burkina Faso a jiya asabar ta bayyana cewa ranar litinin ,gobe kenan za a soma zaman tattaunawa na kasa don tattance wa’adin ko kuma shekaru da majalisar  sojin za ta share  a karagar mulkin kasar kafin daga bisali ta mika mulki ga gwamnatin farrar hula.

Laftana Kanal Paul-Henri Damiba, Shugaban majalisar sojin Burkina Faso
Laftana Kanal Paul-Henri Damiba, Shugaban majalisar sojin Burkina Faso via REUTERS - Burkina Faso Presidency Press Se
Talla

Taron da za a soma gobe litinin zai hada daukacin masu ruwa da tsaki a harakokin siyasa,kungiyoyin farraren hula,wakilan jama’a.

Wasu daga cikin masu zanga-zangar adawa a Burkina Faso
Wasu daga cikin masu zanga-zangar adawa a Burkina Faso AP - Sophie Garcia

Ranar  laraba da ta gabata ne wani kwamity na musaman  da majalisar sojin ta MPSR ta kafa ,ya shawarci sojojin  na ganin sun share watanni 30 a kan karagar mulkin kasar ta Burkina.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.