Isa ga babban shafi

An dage zaman tattaunawa tsakanin gwamnatin Chadi da 'yan Tawaye a Doha

A yau lahadi ya kamata a soma zaman tattaunawa a Doha dake Qatar tsakanin  wakilan majalisar sojin Chadi da shugabanin yan tawaye dake dauke da makamai .

Janar  Azem Bermandoa, mai magana da yahun Gwamnatin Chadi
Janar Azem Bermandoa, mai magana da yahun Gwamnatin Chadi © DJIMET WICHE/AFP
Talla

Wannan zama da aka dage zuwa wani lokaci na a matsayin zakaran gwajin dafi a tsarin da majalisar sojin kasar a karkashin shugabancin Mahamat Idriss Deby Itno na kawo karshen barraka da aka share tsawon shekaru kasar na fama da shi.

Taswirar kasar Chadi
Taswirar kasar Chadi © RFI

Samun nasarar zaman na Doha zai taimaka matuka na ganin an cimma sulhu tsakanin bangarorin da kuma sa ran cimma nasara a taron sulhunta yan kasar ga baki daya watanni goma bayan mutuwar Idriss Deby Itno a fagen daga,wanda bayan haka ne dan sa tareda gundumuwar janar-janar guda 15 na kasar ya sabi  ragamar tafiyar da kasar ta Chadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.